16 Afirilu 2026 - 22:38
Source: ABNA24
Za'a Gudanar Da Tsagaita Wuta Na Kwanaki 10 A Lebanon  A Daren Nan

Iran ta ƙara cin wata nasarar inda ta tilastawa Trump da Isra'ila ayyana tsagaita wuta a Lebanon.

Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Matsayin da Iran ta dauka kan matsayinta na cewa tsagaita bude wuta a kasar Labanon na daya daga cikin muhimman sharuddan duk wani ci gaba a tattaunawar da ake yi da bangaren Amurka da kuma fara tattaunawar zagaye na biyu, ya sa Trump da Isra'ila suka fara bayyana tsagaita bude wuta a daren yau. Isra'ila ta ci gaba da kokarin yin yaki da Lebanon duk da tsagaita wuta da aka yi a Iran, kuma Amurka na kokarin kaucewa wannan batu ta hanyar saba alkawarinta na farko. Amma Iran ta tashi tsaye inda daga karshe ta tilasta wa Trump da Isra'ila yin biyayya ga bukatunta.

Iran ta sake nuna cewa tana tsaye a kan matsayinta kuma ta bijirewa duk wani tilastawa daga ɓangaren Amurka da Isra'ila. kamar yadda Al-Mayadin ta ruwaito, tana mai ambatowa daga majiyoyin Isra'ila: "Kididdiga da aka fitar a wannan gwamnati na nuni da cewa idan aka tsayar da tsagaita bude wuta a kasar Labanon, hakan na nufin ka da bayan Trump kan Iran".

Dan majalisar dokokin kasar Labanon Hassan Fazlullah ya sanar da cewa bangaren Amurka ya yi alkawarin sanar da jami'an Sahayoniyya da shugaban kasar Lebanon matakin tsagaita wuta. Sannan Fazlullah ya jaddada cewa hukumomin Iran za su bi diddigin matakin tabbatauwar Amurka da Isra'ila kan alkawurran da suka dauka na tsagaita wutar domin tabbatar da cewa sun yi shi aikace. Hizbullah a nata bayanin ta ce: Tsagaita wuta ba yana nufin 'yancin gudanar da wani aiki soji da sojojin Isra'ila ba ne domin zata fuskanci hakan da martani mai tsanani kamar yadda Al-Jazeera ta nakalto daga wani babba a kungiyar Hizbullah da bai ambaci sunansa yana cewa ya kamata tsagaita wutar ta hada da dakatar da duk wani matakin soji da ke kai ga ayyukan gaba da juna kan dukkan kasar Labanon. Jami'in na Hizbullah ya bayyana cewa, tsagaita wutar ba zai iya barin wani 'yancin yin aikin soji na Maƙiyiya Isra'ila ba.

Shugaban Amurka ya sanar da cewa tsagaita wuta tsakanin Lebanon da Isra'ila zai fara aiki da tsakar daren yau (Alhamis) na tsawon kwanaki 10. Yayin da rahotanni ke nuna tsagaita bude wuta na wucin gadi a yankin Lebanon, jami'an Isra'ila da kafofin yada labarai sun jaddada cewa sojojin gwamnatin ba su da shirin barin yankunan da aka mamaye a kudancin Lebanon. Jaridar Jerusalem Post ta nakalto wani jami'in Isra'ila yana cewa sojojin "Isra'ila" ta yi niyyar kiyaye matsayinta da mukamanta a kudancin Lebanon a tsawon lokacin dakatar da rikicin. Har ila yau, ma'aikatar rediyo da talabijin ta Isra'ila ta nakalto majiya mai tushe tana cewa firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya yi wani sako karara ga ministocinsa cewa sojojin sahyoniyawan za su ci gaba da zama a kudancin Lebanon kuma ba za su bara wadannan yankuna ba. Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambato wani jami'in Isra'ila yana cewa sojojin ba su da wani shiri na janyewa daga kudancin Lebanon a duk wata yarjejeniyar tsagaita wuta.

Your Comment

You are replying to: .
captcha